BREAKING

Uncategorized

Gobara ta tashi a otal ɗin da ke ɗauke da Alhazan Najeriya 480 a Makkah



Site Subscription Price Supported Countries
FuboTV 5-day free trial, $10–$90/month USA, Canada, Spain
ESPN+ $11.99/month USA
Fanatiz €6.99–€10.99/month Worldwide
StreamLocator 7-day free trial, no credit card required! $9.90/month Worldwide
Advertisement

Gobara ta tashi a otal ɗin Imaratus Sanan da ke birnin Makkah a ƙasar Saudiyya, inda sama da alhazan Najeriya 48 suka sauka yayin aikin Hajjin shekarar 2025.

Otal ɗin yana unguwar Sharamansur a birnin Makkah.

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta tabbatar da cewa dukkanin alhazan sun tsira kuma babu wanda ya ji rauni.

Site Subscription Price Supported Countries
FuboTV 5-day free trial, $10–$90/month USA, Canada, Spain
ESPN+ $11.99/month USA
Fanatiz €6.99–€10.99/month Worldwide
StreamLocator 7-day free trial, no credit card required! $9.90/month Worldwide
Advertisement

A cewar NAHCON, hukumomin gaggawa na Saudiyya da ma’aikatan otal ɗin sun gaggauta kashe wutar kafin ta bazu.

Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Usman, ya ziyarci otal ɗin tare da wasu jami’an hukumar domin duba halin da ake ciki.

Ya bayar da umarnin a kwashe alhazan zuwa wani sabon otal cikin gaggawa, sannan ya yi alƙawarin tallafa musu.

Site Subscription Price Supported Countries
FuboTV 5-day free trial, $10–$90/month USA, Canada, Spain
ESPN+ $11.99/month USA
Fanatiz €6.99–€10.99/month Worldwide
StreamLocator 7-day free trial, no credit card required! $9.90/month Worldwide
Advertisement

“Muna gode wa Allah da babu rai da ya salwanta,” in ji shi.

Ya ce NAHCON za ta yi aiki da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da cewa mahajjatan sun samu kulawa ta musamman.

“An riga an duba sabon wajen da za a sauke su, kuma an fara shirye-shiryen sauya wajen. NAHCON ta kuma yaba da saurin kai taimako da hukumomin Saudiyya da ma’aikatan otal ɗin suka yi.”

Wasu daga cikin mahajjatan sun shaida wa Aminiya cewa gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 12 na ranar Asabar, a lokacin da mafi yawan su ke Mina wajen gudanar da jifar shaiɗan, ɗaya daga cikin manyan ayyukan aikin Hajji.

NAHCON ta ce za ta ci gaba da sanar da al’umma yayin da ake ciki da zarar ta samu sabbin bayanai.


Like this:

Like Loading…

Related Posts